An Kama 'Yar Jarida Zainab Sodiq a Hedikwatar DSS da ke Abuja



Jami'an Hukumar Tsaron Farin Kaya ta Najeriya (DSS) sun kama 'yar jarida Zainab Sodiq, wadda ke bibiyar ayyukan ɗan gwagwarmaya kuma tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa, Omoyele Sowore. A halin yanzu ana tsare da ita a hedikwatar hukumar da ke Abuja.
Rahotanni sun ce kama Zainab ya haifar da damuwa a tsakanin 'yan jarida, ƙungiyoyin fararen hula da magoya bayanta, inda da dama ke kira da a sake ta cikin gaggawa. Lamarin ya kuma sake tayar da muhawara kan 'yancin aikin jarida a Najeriya.

Har zuwa yanzu, ba a bayyana takamaiman dalilin da ya sa aka kama ta ba, kuma DSS ba ta fitar da wata sanarwa a hukumance da ke bayyana musabbabin tsare ta ba.

Post a Comment

Previous Post Next Post