Hukumar zabe Ta Kara Wa'adin Rajista

Hukumar zaben Najeriya wato INEC, ta kara wa'adin dakatar da yin rajistar zabe a duk fadin kasar da makwanni biyu.

INEC, ta ce hakan zai bayar da karin dama ga wadanda ba su samu yin rajistar ba, da kuma wadanda suka cika shekara goma sha takwas, su samu su yin rajistar.

Mai magana da yawun hukumar, Zainab Aminu Abubakar, ta shaida wa BBC cewa, idan ba a manta ba tun a watan Augustan shekarar 2025, INEC, ta fara yin rijistar zabe inda aka yi zango-zango.

Ta ce,"Bisa ka'ida ya kamata ace na dakatar da yin rijistar a ranar 10 ga watan Yulin, 2026, to amma sakamakon bukata daga 'yan siyasa da kungiyoyi masu zaman kansu dama wasu al'umma na kasar da suka bukaci a dan tsawaita lokacin yin rijistar, shi y asa mu dauki wannan mataki."

Post a Comment

Previous Post Next Post