Wata girgizar ƙasa mai ƙarfin maki 7.1 ta afku a kudancin Japan, musamman a yankin Kumamoto, inda ta haddasa ɓarna mai yawa, katsewar wutar lantarki da kuma lalacewar wasu hanyoyi. Girgizar ƙasar ta kuma jawo wata fashewa a wata babbar cibiyar kasuwanci, inda aka ce mutane da dama sun mutu, yayin da wasu kuma suka maƙale a cikin ginin.
Rahotanni sun ce kimanin ma’aikata 20 zuwa 30 ba a samu labarinsu ba a babbar cibiyar kasuwanci ta yankin bayan fashewar da ta faru sakamakon girgizar ƙasar. Tawagogin ceto sun fara aikin neman mutanen da ake kyautata zaton sun makale a cikin ginin da ya lalace.
An kuma ruwaito cewa fiye da mutane 50 sun jikkata a wani asibiti, yayin da wani asibitin ya karɓi kusan mutane 40 da suka samu raunuka, ciki har da 10 da ke cikin mawuyacin hali. Wasu mutane sun kuma jikkata bayan girgizar ƙasar ta sa wani jirgin ƙasa mai saurin gudu ya kauce daga kan layinsa.
Bayan girgizar ƙasar, hukumomin Japan sun fitar da gargadin tsunami, amma daga baya aka janye gargadin. Hukumar kula da makamashin nukiliya ta Japan ita ma ta bayyana cewa ba a gano wata matsala a tashoshin makamashin nukiliya guda uku da ke kusa da yankin ba.
Firaministar Japan Sanae Takaichi ta bukaci mazauna yankunan da abin ya shafa da su koma wuraren da ke da aminci. Ta kuma gargadi jama’a da su kasance cikin shiri, saboda akwai yiwuwar sake samun wata girgizar ƙasa mai irin wannan ƙarfi.
Hukumomi na ci gaba da tantance yawan barnar da girgizar ƙasar ta haddasa, tare da gudanar da aikin ceto da neman mutanen da suka ɓace.