Sanata A Amurka Wanda Ke Goyon Bayan Kasar Israel Lindsey Graham Ya Mutu

Sanatan jam'iyyar Republican mai wakiltar jihar South Carolina a Majalisar Dattawan Amurka, Lindsey Graham, ya rasu yana da shekaru 71 bayan gajeruwar rashin lafiya.

Lindsey Graham

A cikin wata sanarwa da ofishinsa ya fitar a shafukan sada zumunta ranar Asabar, an ce Graham ya rasu ne sakamakon wata "gajeruwa kuma ba zato ba tsammani" rashin lafiya, ba tare da bayyana takamaiman abin da ya yi sanadin mutuwarsa ba.

Sanarwar ta ce iyalansa sun nemi jama'a da su ci gaba da yi musu addu'a tare da girmama sirrinsu a wannan lokaci na jimami.

An zabi Graham a matsayin Sanatan Amurka a shekarar 2002, kuma yana wa'adinsa na hudu yayin da yake neman sake tsayawa takara. Kafin haka, ya taba zama dan Majalisar Wakilai ta Amurka tsakanin shekarun 1995 zuwa 2003.

Ko da yake ya taba neman takarar shugaban kasa a karkashin jam'iyyar Republican a shekarar 2016 tare da sukar Donald Trump a farko, daga baya ya zama daya daga cikin manyan abokan siyasar shugaban Amurkan.

Graham ya kasance daya daga cikin masu bai wa Trump shawara kan harkokin ketare, musamman batutuwan da suka shafi Iran da Rasha. Kwana guda kafin rasuwarsa, ya sanar da cimma yarjejeniya da gwamnatin Trump domin ci gaba da kakaba sabbin takunkumi kan Rasha.

A tsawon rayuwarsa ta siyasa, Graham ya shahara da tsauraran matsayinsa kan manufofin ketare. Ya kasance mai goyon bayan daukar matakai masu tsauri kan Iran tare da mara wa gwamnatin Trump baya kan matakan da ta dauka a rikice-rikicen Gabas ta Tsakiya.

Rasuwarsa na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da tattaunawa kan bukatar kara bayyana gaskiya game da lafiyar 'yan majalisar dokokin Amurka bayan wasu daga cikinsu sun dade suna fama da matsalolin lafiya.

Post a Comment

Previous Post Next Post