Yadda Aka Yi Wa Karnuka Sama Da 400 Kisan Gilla A Habasha

Mazauna garin Hossana, a yankin Tsakiyar Habasha, sun ba da rahoton cewa an kashe ɗaruruwan karnuka bayan jerin hare-haren cizon kare da suka yi sanadiyyar mutuwar wasu mutane a yankin.

Karnuka

Mazauna da jami'ai sun ce kisan ya fara ne bayan mutuwar wasu yara uku sakamakon matsalolin da suka shafi cutar haukar karnuka.

A cewar shaidun gani da ido, wakilan unguwa sun umurci mazauna yankin da su kashe karnukansu ba tare da la'akari da matsayinsu na rigakafi ba.

An ruwaito cewa an tilasta wa masu gidaje su shake dabbobinsu da igiya ko kuma su lakaɗa musu duka har sai sun mutu.

Waɗanda suka ƙi bin umarnin sun fuskanci tarar da ta kai dalar amurka 300.

Wani mazaunin yankin ya shaida wa BBC ba tare da an ambaci sunansa ba cewa kisan ya fara ne bayan da wasu ƴan'uwa biyu suka mutu sakamakon cizon karnuka. "Duk da cewa an yi allurar riga-kafi, wakilan unguwa sun fara aikin kashe dukkan karnuka ba tare da la'akari da yanayin lafiyarsu ba, ko an yi musu allurar riga-kafi ko a'a.

Wani shaida mai suna Alaazar Kebede, wanda likitan dabbobi ne, ya shaida wa BBC cewa, "Duk da cewa an riga an yi allurar rigakafi, wakilan unguwa sun fara yaƙin neman kawar da duk karnukan yankin. An umurci masu karnukan da su kashe dabbobinsu, kuma an kama waɗanda suka ƙi yin hakan. Muna hasashen cewa an kashe karnuka tsakanin 400 zuwa 450 a cikin 'kan kwanaki kaɗan."

"Alaazar ya ƙara da cewa, "Mutane suna jan karnuka suna kashe su ta munanan hanyoyi. Wannan rashin ɗa'a ne kuma ba a yarda da shi ba a addinance, da al'adance, da kuma a fuskar doka.''

Bidiyo ya nuna yadda masu karnukan ke ta sharɓa kuka yayin da ake kashe karnukansu.

Post a Comment

Previous Post Next Post