Gwamnatin Uganda ta fara aikin agajin gaggawa a yankin Karamoja da ke arewa maso gabashin ƙasar, bayan 16 sun mutu sakamakon yunwa da fari mai tsanani da suka addabi yankin.
Firaministar ƙasar, Robinah Nabbanja, ta ce ofishinta zai nemi amincewar majalisar ministoci a ranar Litinin domin sayo ƙarin kayan agaji da za a kai yankunan da fari ya fi shafa.
Manoma sun bayyana cewa sun yi asarar amfanin gona mai yawa bayan watanni da dama na ƙarancin ruwan sama ko rashin samun ruwan sama gaba ɗaya.
Masana sun yi gargaɗin cewa matsalar ƙarancin abinci da ake yawan fuskanta a yankin na faruwa ne sakamakon sauyin yanayi, ƙarancin ruwan sama, sare itatuwa, yawan kiwo fiye da ƙarfin ƙasa, da kuma kwari da ke lalata amfanin gona.