Amurka Ta Sanya Hezbollah a Matsayin Wakiliyar Iran, Ta Kakaba Takunkumi Kan Cibiyar Tallafa Mata Da Kudi

 Amurka ta sake bayyana Hezbollah a matsayin ƙungiyar da ke aiki a matsayin wakiliyar Iran, tare da ƙaƙaba sabbin takunkumai kan wata cibiyar sadarwa da ake zargi da taimaka wa ƙungiyar wajen samun kuɗi.

Ma'aikatar Baitulmalin Amurka ta ce Hezbollah tana aiki ne a ƙarƙashin tasirin Rundunar Kare Juyin Juya Halin Musulunci ta Iran (IRGC), musamman rundunar Quds Force. Amurka ta ce wannan matakin ya nuna yadda take ganin alaƙar aiki, kuɗi da dabaru tsakanin Hezbollah da Iran. 

A wani mataki na daban, Amurka ta sanya mutane 10 cikin jerin waɗanda aka kakaba wa takunkumi saboda zargin hannu a wata hanyar sadarwa da ke tura kuɗaɗe zuwa Hezbollah. A cewar Ma'aikatar Baitulmalin Amurka, hanyar sadarwar tana amfani da masu ɗaukar kuɗi da jiragen fasinja tsakanin Lebanon, Turkiyya, Hadaddiyar Daular Larabawa da Iran, inda ake zargin an rika motsa ɗaruruwan miliyoyin daloli.

Takunkumin na nufin toshe duk wata dukiya da waɗanda aka sanya wa takunkumin ke da ita a ƙarƙashin ikon Amurka, tare da hana 'yan Amurka yin mu'amalar kuɗi da su.

Hezbollah ta yi watsi da matakin, tana mai cewa sabbin takunkumin na Amurka ba za su hana ta ci gaba da abin da ta kira “juriya” ba, kuma ta bayyana dangantakarta da Iran a matsayin wadda take alfahari da ita.

Wannan matakin na Amurka ya zo ne yayin da gwamnatin Shugaba Donald Trump ke ƙara matsa wa Iran lamba ta fuskar tattalin arziki, tare da ƙoƙarin rage hanyoyin da take ganin Iran ke amfani da su wajen tallafa wa ƙungiyoyin da ke da alaƙa da ita a Gabas ta Tsakiya.

Post a Comment

Previous Post Next Post