Biyan Kuɗin NANS Na Shekara Zai Iya Zama Sharadin Shiga Hidimar NYSC

Ƙungiyar Ɗaliban Najeriya (NANS) ta bayyana cewa biyan kuɗin rajista na shekara na naira 200 da take shirin aiwatarwa na iya zama ɗaya daga cikin sharuɗɗan da za a buƙata kafin ɗalibai su samu damar shiga shirin Hidimar Ƙasa (NYSC).

Shugaban NANS na ƙasa, Akinteye Babatunde, ne ya bayyana hakan a wasu saƙonni da ya wallafa a shafinsa na Facebook a ranakun Lahadi da Litinin, inda ya yi bayani kan matsalolin kuɗaɗen ƙungiyar da kuma shirin sauya tsarin karɓar kuɗin rajistarta.

Babatunde ya bayyana cewa NANS na shirin yin aiki tare da NYSC, kuma ɗalibai na iya buƙatar gabatar da takardar shaidar biyan kuɗin NANS kafin a tura su sansanin horo.

Ya ce, “Za mu yi aiki tare da NYSC, kuma ɗaya daga cikin sharuɗɗan shiga sansani shi ne gabatar da rasitin biyan kuɗin NANS.”

Sai dai a wani bidiyo da ya wallafa a ranar Litinin, Babatunde ya bayyana cewa ƙungiyar na nazarin kafa wani tsari da zai ba ta damar karɓar kuɗin rajistarta kai tsaye daga hannun ɗalibai, maimakon dogaro da gwamnatocin ƙungiyoyin ɗalibai (SUG) da kuma shugabannin makarantu.

Ya ce kuɗin rajistar shekara da ake magana a kai naira 200 ne kacal ga kowane ɗalibi.

A cewarsa, sabon tsarin ba wai don ƙara wa ɗalibai nauyin kuɗi ba ne, sai dai domin tabbatar da cewa NANS ta samu isassun kuɗaɗen da za su ba ta damar gudanar da ayyukanta cikin cin gashin kai tare da kare muradun ɗalibai yadda ya kamata.

Ya ce, “Ba don ƙara wa ɗalibai wahala ba ne, domin kuɗin rajistar naira 200 ne kacal ga kowane ɗalibi a shekara.”

Babatunde ya bayyana cewa za a raba kuɗin tsakanin sassa daban-daban na NANS, ciki har da yankuna, jihohi da kuma ƙungiyoyin ɗalibai masu alaƙa da ita.

Ya ce ƙungiyar ta fuskanci matsalar rashin samun kuɗaɗen da ya kamata ta karɓa daga ƙungiyoyin ɗalibai a shekarun baya.

Ya ce, “Muna duba yiwuwar daina dogaro da kuɗaɗen da ake ba mu ta hanyar capitation, mu koma tsarin da za mu karɓi kuɗin kai tsaye daga ɗalibai.”

Shugaban NANS ya yi zargin cewa kusan kashi 80 zuwa 90 cikin 100 na ƙungiyoyin ɗalibai a yanzu ba su da cikakken iko kan kuɗaɗensu, yana mai cewa wasu makarantu suna bai wa ƙungiyoyin ɗalibai kaɗan daga cikin kuɗin da suka tara.

Ya ce hakan ya raunana NANS ta fuskar kuɗi tare da rage ƙarfin da take da shi wajen shiga tsakani a matsalolin da suka shafi ɗalibai.

Babatunde ya kawo misalin Jami’ar Benin, inda ya yi zargin cewa mahukuntan jami’ar sun hana ƙungiyar ɗalibai samun kuɗaɗenta bayan ta yi adawa da ƙarin kuɗin makaranta.

Ya ce, “Ɗaya daga cikin hanyoyin raunana ƙungiya shi ne hana ta kuɗi.”

A cewarsa, duk da matsalolin kuɗi, NANS ta ci gaba da gudanar da ayyukanta, ciki har da ziyartar jami’o’i da shiga tsakani a matsalolin da suka shafi ɗalibai.

Sai dai ya ce ba za a iya sa ran ƙungiyar ta yi tasiri yadda ya kamata ba idan ɗalibai ba sa bayar da gudunmawar kuɗi.

Ya ce, “Ta yaya za ku ji tasirin ƙungiyar yadda ya kamata idan ba ku bayar da gudunmawar kuɗinku ba? Wannan ƙungiya tamu ce baki ɗaya.”

Babatunde ya kuma ce NANS na buƙatar samun ‘yancin cin gashin kanta ta fuskar kuɗi, ba tare da dogaro da ‘yan siyasa ko jami’an gwamnati ba, domin hakan na iya shafar ikon ta na ƙalubalantar hukumomin gwamnati idan bukatar hakan ta taso.

Ya ce, “Ta yaya kuke so mutane su riƙa neman taimakon ‘yan siyasa ko gwamnati, sannan idan suka samu matsala da hukumomin gwamnati, a ce su tsaya su yi yaƙi da waɗannan hukumomin?”

Ya bayyana cewa NANS na tattaunawa da hukumomin da ke hulɗa da ɗalibai domin samar da tsarin da zai ba da damar biyan kuɗin rajistar naira 200 kai tsaye zuwa asusun NANS.

Ya ce, “Muna son haɗa kai da hukumomin da suka shafi ɗalibai domin mu riƙa karɓar kuɗin kai tsaye zuwa ƙungiya, ba ta hannun shugabannin makarantu ko SUG ba.”

Babatunde ya ƙara da cewa NANS za ta gyara kundin dokokinta tare da gabatar da shawarwari domin ba sabon tsarin cikakken goyon bayan doka.

Ya ce, ko da sabon tsarin ba zai amfani shugabancin da yake yi a yanzu ba, yana da tabbacin cewa zai ƙarfafa ƙungiyar ga shugabanni masu zuwa.

Ya ce, “Za mu gyara dokokinmu, mu gabatar da shawarwari daban-daban, sannan mu ga yadda za mu fara karɓar kuɗin rajista kai tsaye zuwa ƙungiyar.”

Babatunde ya kuma bayyana cewa NANS ta karɓi dubban ƙorafe-ƙorafe daga ɗalibai, yana mai cewa ƙungiyar na buƙatar ƙarin ƙarfin kuɗi domin magance irin waɗannan matsaloli.

Ya ce, “A yanzu ina da kusan ƙorafe-ƙorafe 3,000 zuwa 4,000 da ɗalibai suka aiko mana, kuma duk ƙorafe-ƙorafe ne na gaskiya.”

Ya ƙara da cewa a baya NANS ta kashe kuɗi wajen taimaka wa ɗalibai a lokutan gaggawa, ciki har da lokutan da aka yi garkuwa da wasu ɗalibai, da kuma haɗurran motocin ƙungiyar.

Ya ce, “Daga ina ake samun waɗannan kuɗaɗen, alhali ƙungiyar ba ta da tsarin karɓar kuɗin rajista yadda ya kamata?”

Sai dai duk da kalaman Babatunde da ke nuna cewa NANS na nazarin haɗa biyan kuɗin rajista da tsarin tura ɗalibai NYSC, bai bayyana yadda za a aiwatar da wannan tsari ba ko kuma lokacin da zai fara aiki.

A halin yanzu, NYSC na da sharuɗɗa da hanyoyin tura masu hidima da doka ta tanada, kuma duk wani sabon sharadi da ya shafi kuɗin NANS sai an kafa shi a hukumance kafin ya zama wajibi.

Babatunde ya jaddada cewa manufar sabon tsarin biyan kuɗi kai tsaye ita ce tabbatar da cewa NANS ta samu cikakken ‘yancin cin gashin kanta ta fuskar kuɗi, tare da ƙara ƙarfafa ikon ta na kare muradun ɗaliban Najeriya.

Ya ce, “Ba don matsa wa ɗalibai lamba ba ne, sai dai domin a yi abin da ya dace, ta yadda ƙungiyar za ta iya cin gashin kanta kuma ta gudanar da ayyukanta yadda ya kamata.”

Post a Comment

Previous Post Next Post