Liverpool da Man City Sun Fuskantar Sabuwar Rayuwa Ba tare da Salah da Guardiola ba

Mohamed Salah da Pep Guardiola na daga cikin fitattun mutane a tarihin gasar Premier League, kuma yadda Liverpool da Manchester City za su iya ci gaba ba tare da su ba zai taka muhimmiyar rawa wajen tantance irin kakar da kungiyoyin biyu za su yi.A karon farko tun daga shekarar 2016, Liverpool za ta fara kakar wasa ba tare da ɗan wasan Masar, Salah, a matsayin jagoranta ba. Haka kuma, Manchester City ba za ta ƙara dogaro da dabarun Guardiola ba, bayan kocin ya kawo ƙarshen shekaru goma masu cike da nasarori a ƙungiyar.

Salah ya koma kulob ɗin Trabzonspor na Turkiyya a farkon watan Agusta, lamarin da ya kawo ƙarshen zamansa a Anfield, inda ya kafa tarihi a matsayin ɗaya daga cikin manyan ‘yan wasan da suka taɓa taka leda a tarihin Liverpool.

Guardiola kuwa ya yi murabus a ƙarshen kakar wasan da ta gabata, inda ya kawo ƙarshen mafi kyawun zamani a tarihin Manchester City. Yanzu ƙungiyoyin biyu sun shiga sabon zamani ba tare da manyan jagororinsu ba, yayin da sabuwar kakar Premier League ta fara.

Manchester City za ta karɓi bakuncin Bournemouth ranar Lahadi a wasan farko na Enzo Maresca a matsayin magajin Guardiola. Bayan sa’o’i kaɗan, sabon kocin Liverpool, Andoni Iraola, zai jagoranci ƙungiyarsa a wasan da za ta ziyarci Newcastle, ba tare da Salah ba.

Rashin tabbas game da makomar Liverpool da City a wannan kakar ba ya samo asali ne kawai daga rashin Guardiola da Salah ba, har ma da rikice-rikicen da suka gabaci rabuwar su da ƙungiyoyin a watan Mayu.

Guardiola ya lashe kofunan Premier League guda shida da kuma gasar Zakarun Turai ta farko a tarihin Manchester City, cikin kofuna 20 da ya lashe tun bayan da ya karɓi ragamar ƙungiyar a shekarar 2016.

Kocin mai shekaru 55 ya kuma lashe FA Cup da League Cup a kakar wasansa ta ƙarshe, amma ya bar City a lokacin da ƙungiyar ta rasa matsayin da take da shi na kasancewa mafi ƙarfi a ƙwallon ƙafa ta Ingila, bayan da ta kasa lashe Premier League a shekaru biyu na ƙarshe na mulkinsa.

Guardiola ya amince cewa ya sha wahala wajen samar da kuzarin da ake buƙata domin jagorantar City wajen fafatawa da Arsenal a kakar da ta gabata. Daga ƙarshe Arsenal ta kammala kakar wasan da tazarar maki bakwai, inda ta lashe gasar.

Ficewar daraktan wasanni da Guardiola ya dogara da shi, Txiki Begiristain, a shekarar 2025, ta ƙara masa damuwa, inda ya bayyana cewa, “wani ɓangare na ni yana tafiya.”

Bugu da ƙari, City na fuskantar tuhumar Hukumar Kwallon Ƙafa ta Ingila kan zargin karya dokokin kuɗi, lamarin da ya daɗe yana ci gaba ba tare da an yanke hukunci a kai ba. Hakan ya sa Guardiola ya ji cewa dole ne ya ci gaba da kasancewa mai biyayya ga ƙungiyar.

Sai dai a hankali ya fara bayyana gajiyarsa sakamakon nauyin sake gina ƙungiyar da ke buƙatar sabbin ‘yan wasa, bayan ficewar wasu fitattun ‘yan wasanta da suka haɗa da Kevin De Bruyne, Ederson, Kyle Walker da Riyad Mahrez a shekarun baya.

Sabon shirin sake gina City da aka kashe makudan kuɗaɗe a kansa ya samu nasara kaɗan ne kawai, abin da ya bar tsohon kocin Chelsea, Maresca, da babban ƙalubale na ci gaba da gadon Guardiola.

Maresca ya san City sosai, domin ya taɓa kasancewa mataimakin Guardiola a kakar 2022/23, wadda City ta lashe kofuna uku.

Sai dai ƙwarewar Maresca a matsayin babban koci ba ta kai ta Guardiola ba. Ya shafe ƙasa da shekaru biyu a Chelsea, shekara guda a Leicester City a mataki na biyu, sannan ya yi ɗan gajeren zama a Parma.

Tarihin Maresca mai ƙarancin nasarorin koci ya sha bamban ƙwarai da na Guardiola, wanda ya riga ya tara manyan kofuna a Barcelona da Bayern Munich kafin ya koma Manchester.

A gefe guda kuma, Liverpool na fara ɗaukar matakan farko zuwa sabon zamani ba tare da Salah ba.

Lokacin da Salah ya koma Liverpool daga Roma kan fan miliyan 36 a shekarar 2017, da wuya mutane su yi hasashen irin gagarumar nasarar da zai samu a Anfield.

Salah ya taɓa samun matsala a lokacin da yake Chelsea, amma da zarar ya koma Liverpool, ya zama babban jigo a ƙungiyar.

Dan wasan mai shekaru 34 ya zura ƙwallaye 257 a wasanni 442 da ya buga wa Liverpool a dukkan gasa, abin da ya sanya shi zama na uku a jerin waɗanda suka fi zura ƙwallaye a tarihin ƙungiyar.

Ya samar da lokuta masu ban mamaki da dama, yayin da ya taimaka wa Liverpool lashe kofunan Premier League guda biyu, Champions League, FA Cup da League Cup.

Sai dai ƙarshen zamansa a Liverpool bai kasance cikin yanayi mai daɗi ba.

An rage masa damar buga wasa sau da dama a ƙarƙashin Arne Slot a kakar da ta gabata, sannan Salah ya zargi ƙungiyar da “jefa shi ƙarƙashin mota” bayan rikicin da ya shiga da ita.

Rikicin da ke tsakanin Salah da Slot bai taɓa warwarewa gaba ɗaya ba, kuma Salah ya zura ƙwallaye bakwai kacal a gasar Premier League, yayin da Liverpool ta kammala kakar a matsayi na biyar kafin daga bisani a sallami kocin ɗan ƙasar Netherlands.

Sauya ɗan wasa mai irin girman Salah ba abu ne da za a iya yi cikin sauƙi ta hanyar ɗaukar ɗan wasa guda ɗaya ba.

Iraola zai yi fatan ɗan wasan Sweden, Alexander Isak, zai inganta sosai bayan kakarsa ta farko a Anfield wadda rauni ya kawo cikas. Sabon ɗan wasa Victor Munoz da matashin Rio Ngumoha su ma na fuskantar babban fata daga magoya bayan ƙungiyar.

Sai dai duk ƙoƙarin da Liverpool da Manchester City za su yi, babu makawa ƙungiyoyin biyu za su kasance da wani sabon salo bayan rabuwarsu da waɗannan manyan gumakan da suka ayyana zamaninsu.

Post a Comment

Previous Post Next Post