Wasu ma’aikatan filin jirgin sama a Jamus sun mutu sakamakon kamuwa da zazzabin cizon sauro (malaria) da ake zargin wani sauro da ya shigo cikin jirgin sama ne ya haifar.
Rahotanni sun ce sauro mai ɗauke da kwayar cutar ya shiga cikin jirgin daga wani yanki da malaria ke yaduwa, sannan ya ciji mutane bayan jirgin ya isa Jamus.
Lamarin ya jawo damuwa kan yiwuwar sauro masu ɗauke da cututtuka su yi tafiya ta jiragen sama daga ƙasashe masu fama da malaria zuwa ƙasashen da cutar ba ta yawan faruwa.
Hukumomi da masana kiwon lafiya na binciken lamarin tare da ɗaukar matakan da suka dace domin hana ƙarin kamuwa da cutar.