Hausawa Na Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Hadin Kai da Ci Gaban Najeriya - Bola Tinubu

Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya bayyana al’ummar Hausawa a matsayin ginshiƙai masu muhimmiyar rawa wajen tabbatar da haɗin kan ƙasa da ci gaban Najeriya.

Bola Ahmed Tinubu

Tinubu ya ce al’ummar Hausawa na taka muhimmiyar rawa wajen ƙarfafa haɗin kai da kuma bunƙasa ci gaban ƙasar.

Shugaban ya kuma bayyana cewa harshen Hausa ya samu gagarumar bunƙasa, inda ya zama ɗaya daga cikin manyan harsunan haɗin kai da kasuwanci a Najeriya da sauran sassan duniya.

Tinubu ya bayyana hakan ne a cikin saƙon taya murnar Ranar Hausa, wadda ake gudanar da bikin cikinta a yau a fadar Sarkin  Daura.

Ya ce: “Ina taya ɗimbin al’ummar Hausawa murnar Ranar Hausa, wadda ake bikin ta a yau a fadar tarihi ta Daura.”

Shugaban ya kuma yaba wa al’ummar Hausawa bisa irin gudunmawar da suke bayarwa wajen tabbatar da haɗin kan Najeriya da ci gabanta.

Post a Comment

Previous Post Next Post