Firaministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu, ya kira Birtaniya da kalmar “Jamhuriyar Musulunci ta Birtaniya” a wata hira da aka yi da shi a gidan rediyon sojojin Isra’ila. Ya yi hakan ne yayin da yake sukar yadda kafafen yaɗa labarai na Birtaniya ke ɗaukar labaran Isra’ila.
Netanyahu ya kwatanta Birtaniya ta yau da yadda take a baya, yana mai yaba wa marubuci Randolph Churchill, ɗan tsohon Firaministan Birtaniya Winston Churchill, saboda irin rahotannin da ya taɓa rubutawa game da Isra’ila a lokacin Yaƙin Kwanaki Shida na 1967.
Ya kuma yi wata magana mai alaƙa da makaman nukiliya, inda ya ce an taɓa cewa Birtaniya na iya zama “jamhuriyar Musulunci ta farko da ta mallaki makaman nukiliya”. Wannan magana ta jawo suka daga wasu ƙungiyoyin Yahudawa a Birtaniya da kuma 'yan siyasa.
Maganar ta zo ne a lokacin da dangantakar Birtaniya da Isra’ila ke ƙara yin tsami. Gwamnatin Birtaniya ta ɗauki wasu matakai kan Isra’ila, ciki har da takunkumi kan wasu jami’an Isra’ila da kuma matakan da suka shafi makamai da matsugunan Yahudawa a yankunan da aka mamaye.
Wasu masu suka sun bayyana kalaman Netanyahu a matsayin rura ƙiyayya da Musulmi da kuma furucin da zai iya ƙara rarrabuwar kawuna. Ƙungiyar Yahudawa ta Progressive Judaism a Birtaniya ta kuma jaddada cewa Netanyahu ba ya magana a madadin Yahudawan Birtaniya.