Majalisar Shura ta jihar Kano, ƙarƙashin jagorancin sakataren majalisar kuma Kwamishinan kasuwanci na Kano Alhaji Shehu Wada Sagagi ya tabbatar da cewa, ƙungiyoyin addini da al'umma takwas (8) ne suka shigar da ƙorafe-ƙorafe bayan amsa kiran mai girma Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf na cewa, duk mai ƙorafi ya kawo a rubuce.
Majalisar ta gayyaci Sheikh Abubakar Shu'aibu Lawal limamin masallacin Triumph, a kan ƙorafe-ƙorafen da aka shigar a kansa ana zarginsa da ya yi ɓatanci ga fiyayyen halitta Annabi Muhammad (S.A.W.) a karatunsa da ya gabata.
Haka nan, su ma waɗanda suka shigar da ƙorafe-ƙorafen majalisar ba ta yi ƙasa a gwiwa ba, sai da ta gayyace su, domin jin ta bakin kowanne daga cikinsu.