Ƙarƙashin umarnin Shugaban Ƙasa Bola Ahmad Tinubu, mataimakinsa, Kashim Shettima, zai jagoranci tawagar Najeriya zuwa taron shugabannin ƙasashe karo na tamanin (80) na Majalisar Ɗinkin Duniya, wanda zai gudana a birnin New York na ƙasar Amurka.
Taron zai kasance daga ranar 22 zuwa
28 ga Satumba, inda shugabannin ƙasashen duniya za su halarta domin tattaunawa
da kuma muhawara kan muhimman batutuwa na duniya.
A cewar mai magana da yawun
mataimakin shugaban ƙasa na musamman kan harkokin yada labarai, Stanley Nwocha,
ana sa ran Shettima zai halarci taron tun daga ranar 22 ga Satumba, tare da
sauran shugabannin ƙasashe, domin taron bude baki da kuma tattaunawar da za ta
gudana daga 22 zuwa 28 ga watan.
Kamar yadda jaridar The Nation ta ruwaito.
