Hukumar Kula da Makamai (DICON) Ta Tabbatar Mutuwa a Fashewa a Kaduna, Ta Kwantar da Hankali

Hukumar ƙera makamai ta ƙasa, Defense Industries Corporation of Nigeria (DICON), ta tabbatar da mutuwar wani ma’aikaci sakamakon fashewar wani abu a wurin aiki da ke garin Kaduna.

Lamarin ya faru ranar Asabar misalin ƙarfe 10:00 na safe, a yayin da ma’aikatan ke ƙoƙarin lalata wasu tsofaffin makamai da wasu sinadaran ƙera makamai - ciki har da ammonium nitrate, primer caps, propellants, da sauran kayan haɗi. Wani ɓangare na aikin ya tashi aiki wanda ya haifar da fashewar.

Hukumar Kula Da Makamai

Mai magana da yawun hukumar, Maria Sambo, ta ce an garzaya da waɗanda suka ji rauni zuwa Asibitin Sojoji na 44, Kaduna, domin samun kulawar likitoci. Ta ƙara da cewa gawar mamacin an kai ta zuwa ɗakin ajiye gawuna (mortuarium).

Sambo ta yi kira ga mazauna unguwar Kurmin Gwaro da kewaye da su kwantar da hankalinsu, tana mai cewa an ɗauki dukkan matakan tsaro kuma babu wani tashin hankali a yankin. Ta tabbatar wa al'umma cewa hukumar ta ƙaddamar da ƙwararrun matakan kariya ga mazauna da ke makwabtaka da ma’aikatar.

Hukumar ta sanar cewa an naɗa kwamitin bincike domin gano musabbabin fashewar, kuma ana ci gaba da aiki tukuru don tabbatar da cikakken bincike da kuma ɗaukar darasi daga abin da ya faru.

Abu-Ubaida Sani

I provide language services such as translation, transcription, proofreading, interpretation, etc in the Hausa language. I also outsource in Pidgin, Yoruba, Igbo, Fulah, and Kanuri. Contact me through email: abuubaidasani5@gmail.com or WhatsApp: +2348133529736

Post a Comment

Previous Post Next Post