Majalisar Wakilai Ta Bukaci A Hukunta Kamfanonin Da Ke Kin Bin Dokar Inshorar Lafiya

Majalisar Wakilai ta Tarayya ta ɗauki mataki domin tilasta wa kamfanonin masu zaman kansu bin Dokar Inshorar Lafiya ta Ƙasa (NHIS), wadda ta wajabta inshorar lafiya ga dukkan ma’aikata da ke aiki a kamfanonin da ke da ma’aikata fiye da biyar.

RepsWannan matakin ya biyo bayan ƙuduri da Hon. Felix Uche Nwaeke (PDP, Rivers) ya gabatar a zaman majalisar na jiya (Alhamis), wanda aka amince da shi bayan tattaunawa mai zurfi.

A cewar Nwaeke, Dokar Inshorar Lafiya ta Ƙasa ta 2022 ta tanadi cewa duk ma’aikaci a kamfanin da ke da ma’aikata sama da biyar dole ne a haɗa shi cikin tsarin inshorar lafiya.

Ya bayyana cewa Hukumar Kula da Inshorar Lafiya ta Ƙasa (NHIA) ce ke da alhakin ba da lasisi da sa ido kan ƙungiyoyin Health Maintenance Organisations (HMOs), domin tabbatar da bin ƙa’idoji da samun damar daidaitacciyar kulawar lafiya ga ma’aikata a fannoni biyu gwamnati da masu zaman kansu. 

Dan majalisar ya kuma yi bayanin cewa, bisa ga tanadin doka, kamfani na da alhakin biyan kashi 10% na albashin ma’aikaci, yayin da ma’aikaci zai biya kashi 5%, wanda ke zama jimillar kashi 15% na albashin tushe.

Sai dai Nwaeke ya nuna damuwa cewa kamfanoni da dama ba sa yin rijista da tsarin, kuma ba sa biyan gudunmawar da doka ta tanada, abin da ke barin ma’aikata cikin hali na rashin taimako lokacin da suka kamu da rashin lafiya.

Ya ce wannan rashin bin doka na kawo cikas ga manufar gwamnati ta samar da ingantaccen tsarin inshorar lafiya ga dukkan ’yan ƙasa, musamman ma’aikatan da ke fuskantar matsin tattalin arziki.

Daga karshe, Majalisar ta buƙaci Hukumar NHIA da ta fara tattara bayanai kan dukkan kamfanonin da ke karya dokar tare da daukar matakin ladabtarwa a kansu.

Haka kuma ta umarci Kwamitin Majalisa kan Harkokin Lafiya da ya tabbatar da bin wannan doka yadda ya kamata, tare da miƙa rahoto cikin makonni hudu domin ɗaukar ƙarin matakin majalisa.

Post a Comment

Previous Post Next Post