Wata kotu A Abuja Ta Umurci Wani Da Ya Biya Hukumar DSS Diyyar Naira Biliyan Biyar (5m)

Kotun Babban Birnin Tarayya ta umurci wani mutum mai suna Sunday Dominic da ya biya Hukumar Tsaro ta Kasa (DSS) tarar naira miliyan biyar (₦5m) a matsayin diyya ta ladabtarwa saboda shigar da ƙara marar tushe da ta’ammali da hujjoji marasa tabbas kan hukumar tsaro.
A cikin hukuncin da aka yanke kan shari’ar da ke da lamba FCT/HC/CV/3984/2024, Mai Shari’a A.Y. Shafa ya bayyana cewa Dominic bai nuna hujjar da ke tabbatar da cewa DSS ta tauye masa haƙƙinsa na dan Adam ba, lokacin da aka gayyace shi don bincike kan wasu zarge-zargen damfara. Bayan nazarin hujjojin da ɓangarorin biyu suka gabatar, alkalin ya yi watsi da ƙarar bisa rashin cancanta, tare da bayyana ta a matsayin ƙara marar tushe kuma banza.

Dominic ya nemi kotu ta ayyana cewa DSS ta take masa haƙƙin rayuwa, mutunci da ’yancin kansa, tare da buƙatar diyya ta ₦10 miliyan. Sai dai Mai Shari’a Shafa ya yanke hukuncin cewa hukumar ta DSS ta yi aikinta ne bisa ikon da doka ta ba ta, kuma babu wata take haƙƙi da aka aikata masa.

Da yake mayar da martani kan hukuncin, wani babban lauya ya yaba da hukuncin, yana mai cewa wannan mataki ne na tarihi da zai ƙarfafa ikon hukumomin tsaro wajen gudanar da ayyukansu na doka ba tare da tsangwama ba.

“Wannan hukunci ya tabbatar da ƙa’idar cewa dole ne a bar hukumomin tsaro su gudanar da aikinsu ba tare da tsoron shigar da ƙararraki marasa tushe ba,” in ji lauyan. “Idan jami’an tsaro ba za su iya gayyatar mutum don tambayoyi ba, hakan zai hana su gudanar da aikin kare tsaro da aiwatar da doka.”

Masu lura da harkokin shari’a sun bayyana cewa wannan hukunci zai zama gargaɗi ga masu shigar da ƙararraki marasa tushe da ke nufin tsoratar da hukumomin tsaro da kuma hana adalci gudana yadda ya kamata.

Post a Comment

Previous Post Next Post