An Kona Uwargida Da Amarya A Gidan Aurensu A Kano

Rundunar ƴansandan jihar Kano ta ce tana binciken domin gano waɗanda ake zargi da hallaka wasu matan aure - uwargida da amarya - ta hanyar cinna musu wuta a ɗakunan aurensu.

Lamarin ya auku ne ranar Alhamis da rana, lokacin da maigidan baya nan kuma babu zirga-zirgar mutane a unguwar.

Al'amrin ya faru ne a unguwar Tudun Yola cikin ƙaramar hukumar Gwale da ke tsakiyar birnin na Kano.

CSP. Abdullahi Haruna Kiyawa ya tabbatar wa BBC faruwar lamarin, inda ya ce ba zai faɗaɗa bayani ba, "don kada a samu matsala a binciken" da suke yi.

Kakakin ƴansandan ya ce jami'ansu sun gano wasu wayoyin hannu guda biyu - da suke tsammanin na waɗanda suka aikata laifin ne.

CSP Kiyawa ya ƙara da cewa sun kuma fahimci cewa maharan sun jikkata uwargidan kafin su banka mata wuta.

Post a Comment

Previous Post Next Post