Tinubu Ya Tsawaita Wa'adin Buba Marwa A Shugabancin NDLEA

Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu ya tsawaita wa'adin Buba Marwa a matsayin shugaban hukumar NDLEA mai yaƙi da Sha da fataucin kayan maye a ƙasar.

Cikin wata sanarwa da fadar shugaban ƙasar ta fitar a ranar Juma'a, ta ce Shugaba Tinubu ya amince da da ƙarin wa'adin shekara biyar ga Buba Marwa.

Tsohon shugaban Najeriya, Marigari Muhammadu Buhari ne ya fara naɗa Buba Marwa a watan Janairun 2021.

Amincewa da tsawaita wa'adin Marwa - wanda tsohon gwamnan soji na jihohin Lagos da Borno ne - na nufin zai kasance shugaban hukumar NDLEA har nan da 2031.

Post a Comment

Previous Post Next Post