'Isra'ila Ta Kashe Akalla Mutum 11 A Gaza'

Jami'an kungiyar samar da tsaro ga fararen hula ta Hamas a Gaza sun ce hare-haren da Isra'ila ta kai a Gaza sun kashe akalla mutun sha daya.

Kakakin kungiyar ta Civil defense a Gaza ya shaidawa BBC cewa mutum biyar ciki har da mata da kananan yara ne suka mutu a yayin harin da Israilar ta kai a wurin ibada sai kuma karin wasu mutu uku da suka mutu.

An kai harin ne a wani filin wasa da Majalisar Dunkin Duniya ke tafiyarwa a birnin na Gaza.

Sojojin Isra'ila sun kai harin ne a wani wuri da ta kira maboyar 'yan ta'adda a Gaza bayan da mayakan Hamas suka bude musu wuta a yankin Khan Younis.

Post a Comment

Previous Post Next Post