Me ya sa Shugaban Iran ya Nemi Afuwar Makwaftan ƙasar?

Shugaban ƙasar Iran Masoud Pezeshkian ya bai wa mutane da dama mamaki bayan ya nemi afuwar maƙwaftan ƙasar bisa ga hare-haren da ƙasar ta ƙaddamar a cikinsu.

Shugaban ya nemi afuwar ne a ranar Asabar, a matsayinsa na ɗaya daga cikin mambobin kwamitin riƙon-ƙwarya na jagorancin ƙasar.

Abu ne mai wahala wata ƙasa ta nemi afuwar wata, musamman a alokacin da ake gwabza yaƙi, haka nan ma kalmomin da ya yi amfani da su, sun ɗauki hankali.

A mafi yawan lokuta da wahala ka ga shugabanni sun yi amfani da kalamar "nadama", sannan kuma ba su cika ɗaukan alhaki ba kai-tsaye.

Amma shi Pezeshkian kai-tsaye ya amince cewa an kai farmaki kan ƙasashe masu maƙwaftaka sannan ya ce a yanzu an buƙaci dakaru su tsagaita daga kai musu hari har sai idan daga cikin ƙasashen ne aka kai wa Iran hari.

"Na ga dacewar na nemi afuwar ƙasashe maƙwafta waɗanda aka kai wa hari," in ji shi. "Ba aniyarmu ba ne mu far wa maƙwaftanmu."

To sai dai tambayar ita ce: shin wannan neman afuwa ta kai zuci, kuma me ya sa sai yanzu?

Wata ƙila mataki ne na shugabancin ƙasar wajen ganin yankin bai hargitse ba.

Post a Comment

Previous Post Next Post