Matashi Ya Rubuta Littafi Yana Bayyana Labaran Da Ba a Ji Ba Na Kisan Kare-Dangi Da Isra’ila Ke Yi a Gaza

 Wani matashi ɗan Gaza ya wallafa sabon littafi da ke tattara labaran rayuwa daga wajen da ake fama da yaƙi, yana bayyana abubuwan da suke faruwa a zahiri a lokacin da Isra’ila ke aiwatar da kisan ƙare-dangi a yankin.

kisan ƙare-dangi

Littafin, wanda matashin ya ce ya ginu ne kan shaida kai tsaye, hotuna, da labaran waɗanda suka tsira, yana nuni da irin wahalar da fararen hula ke fuskanta, daga kashe-kashe, rugujewar gidaje, yunwa zuwa rashin magani.

Ya ce burinsa shi ne ya tabbatar duniya ta ga gaskiyar abin da ke faruwa a Gaza, ba wai abin da ake nuna wa al’umma a taƙaice ba.

Littafin ya fara samun karɓuwa a shafukan sada zumunta, inda mutane da dama ke yaba kwazon matashin wajen adana tarihin Gaza a lokacin da ake ƙoƙarin murkushe shi.

Post a Comment

Previous Post Next Post