Turkiyya Ta Bada Umarnin Kama Firaministan Israel Benjamin Netanyahu

Masu shigar da ƙara a Turkiyya sun bayar da sammacin kama Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu da ministan tsaro da wasu jami'ai 35.

Benjamin Netanyahu

Ofishin mai shigar da ƙara na birnin Istanbul ya ce ana neman mutane ne bisa laifukan yaƙi da kisan ƙare-dangi da suka aikata a zirin Gaza, da wani jirgin kayan agaji.

Isra'ila ta sha musanta zargin aikata laifukan kisan ƙare-dangi a Gaza.

Matakin na Turkiyya na zuwa ne yayin da Shugaban Amurka Donald Trump ke kambama rawar da Turkiyyan ta taka wajen ƙulla yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin Hamas da Isra'ila.

Kazalika, Turkiyyar na shirin tura dakaru domin aiki da takwarorinsu wajen kiyaye zaman lafiya a Zirin Gaza.

Post a Comment

Previous Post Next Post