An Maye Gurbin Ahmed Farouk Da Sa'idu Aliyu Muhammad Daga Jihar Gombe

Jim kaɗan bayan sanar da murabus da Ahmed Farouk ya yi daga shugabancin hukumar kula da harkokin sarrafawa da tacewa da sufurin man fetur a Najeriya NMDPRA, shugaba Bola Tinubu ya aike da sunan mutumin da zai gaje shi.

A wata sanarwa daga fadar shugaban ƙasar mai dauke da sa hannun mataimaki na musamman kan harkokin yada labarai, Bayo Onanuga ya ce shugaba Tinubu ya nemi majalisar dattawa da ta amince da naɗin da ya yi wa Injiniya Sa'idu Aliyu Mohammed a matsayin sabon shugaban NMDPRA.

An haifi Injiniya Sa'idu a 1957 a garin Gombe da ke jihar Gombe da ke arewa maso gabashin Najeriya.

Injiniya Sa'idu Aliyu Mohammed ya kammala digirinsa na farko a 1981 daga jami'ar Ahmadu Bello da ke Zaria, inda ya karanci fannin injiniyan sinadarai.

Post a Comment

Previous Post Next Post