Wata Sabuwa: Kotun Koli Ta Baiwa Tinubu Damar Tube Zababbun Gwamnoni

Tun bayan da kotun ƙoli ta bai wa shugaban Najeriya, Bola Tinubu ƙarfin ayyana dokar ta-ɓaci a kan jihohi da ma ikon tuɓe zaɓaɓɓen gwamna da ƴanmajalisa, ƴan Najeriya ke ta bayyana ɗarɗar dangane da ƴancin zaɓaɓɓun shugabanni a jihohi.

A ranar Litinin ɗin da ta gabata ne dai Kotun Ƙolin Najeriyar ta yanke hukunci cewa shugaban ƙasa na da ikon dakatar da zaɓaɓɓen jami'in gwamnati a lokacin da aka ayyana dokar ta-ɓaci a wata jiha.

Kwamitin alƙalai bakwai ne dai suka yanke hukuncin, inda shida daga ciki suka amince da matsayar kotun, yayin da alƙali guda ɗaya ya bayar da ra'ayi na daban.

Wannan hukunci ya zo kusan watanni uku bayan an kawo ƙarshen dokar ta-ɓaci a jihar Rivers tare da mayar da gwamnan da majalisar jihar kan mukamansu.

Post a Comment

Previous Post Next Post