Wata Kotu ta Mika wa EFCC Kadarorin Malami

Wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a Abuja ta bayar da umarnin wucin-gadi na ƙwace kadarori 57 na tsohon ministan shari'a na Najeriya, Abubakar Malami.

Kotun ta yanke hukuncin ne a ranar Laraba, inda ta ce kadarorin mallakin Malami da ƴaƴansa biyu - Abdulziz Malami da Abiru-Rahman Malami ne, kuma tana zargin an mallake su ne ta hanyar da ba ta dace ba.

Mai shari'a Emeka Nwite ne ya yanke hukuncin, bayan lauyan hukumar EFCC, Ekele Iheanacho ya buƙaci hakan.

A wata sanarwa da EFCC ta fitar, ta ce an ƙiyasta darajar kadarorin za ta kai naira N213,234,120,000, waɗanda ta ce ya mallaka a jihohin Kebbi da Kano da Kaduna da Abuja.

Post a Comment

Previous Post Next Post