Mutane da yawa suna yawan magana a kan rabuwar kan Musulmi, suna koka cewa; Musulmai sun rabu gida - gida, akwai 'Yan Izala, 'Yan Darika har an samu 'Yan Shi'a da Khawarijawa, irin 'Yan Boko Haram da makamantansu.
Abin mamaki, cikin masu korafi a kan rarrabuwar Musulmi, har da
'Yan Boko Aqida. Sai ka ji yana korafi, yana zagin Musulmai, yana siffanta su
da munanan siffofi, saboda sun rabu kungiyoyi. Sai ka ji yana cewa: Ni kawai
Musulmi ne, ba ruwana da kowace kungiya. Ai kowace kungiya tsarkake kanta take
yi tana cewa; ita ce 'yar Aljanna. Yana wadannan surutai alhali yana cikin
manyan masu raba kan Musulmai. Saboda babu wani sababi na rabuwar kai face yana
aikatawa, kuma yana kira ga aikatawan.
Daga cikin wadannan sabuba akwai:
1- Sabon Allah: Lallai lokacin da al'umma ta yi dumu-dumu cikin
sabon Allah to dole za a rasa soyayya a tsakaninsu, sai rarrabuwa ya afku a
cikinsu. Saboda Imani da kyawawan aiyuka da da'a ma Allah su suke sa Allah ya
sanya soyayya tsakanin bayi. Allah ya ce:
{إِنَّ
الَّذِينَ آمَنُوا وَعَمِلُوا الصَّالِحَاتِ سَيَجْعَلُ لَهُمُ الرَّحْمَنُ
وُدًّا} [مريم: 96]
"Lallai wadanda suka yi imani, suka aikata aiyuka na gari
Allah Mai rahma zai sa a so su".
2- Bidi'a: Lallai kirkirar Bidi'a a cikin Addini da bin
tafarkin Bidi'a, da saba tafarkin Manzon Allah (saw) da Sahabbansa yana lazimta
rarrabuwar al'umma. Hakan ya tabbata a Hadisin da Annabi (saw) ya ba da labarin
rarrabuwar al'ummarsa kashi 73, wanda rabuwa da tafarkin Sunnar Annabi (saw)
shi ya janyo wannan rarrabuwar.
3- Munanan halaye da munanan dabi'u: Duk lokacin da mutane suka
zama marasa mutunci a tsakaninsu, suna mu'amalantar juna da munanan halaye da
miyagun dabi'u, to dole su rarrabu kashi - kashi. Wannan ya sa Annabi (saw) ya
hane mu ga munanan halaye inda ya ce:
«إياكم والظن، فإن الظن أكذب الحديث، ولا
تحسسوا، ولا تجسسوا، ولا تناجشوا، ولا تحاسدوا، ولا تباغضوا، ولا تدابروا، وكونوا
عباد الله إخوانا»
صحيح
البخاري (8/ 19)، صحيح مسلم (4/ 1985)
"Kar ku yi mummunan zato, kar ku yi sa ido, kar ku yi
tajassusi, kar ku yi najashu a kasuwanci, kar ku yi hasada, kar ku yi kiyayya,
kar ku juya baya wa juna, kar wani ya yi ciniki a kan cinikin dan uwansa, kar
ku yi gasa a junanku".
To in ka duba wadannan duka za ka ga 'Yan Boko Aqida sun fi
kowa sabon Allah da halasta saba masa, da yakar masu hani a kan aikata sabo da
sunan 'yanci. Sun fi kowa Bidi'a da dauko tunanin 'Yan Bidi'ar, da kare su.
Haka sun fi kowa munanan halaye da cin mutuncin mutane. A ko'ina wadannan su ne
manyan halayensu.
Saboda haka in da gaske muke yi, muna son hadin kan Musulmi, to
sai mun nisanci sabon Allah ta kowace fiska, mun nisanci Bidi'ao'in da aka
shigo da su cikin Addini, Bidi'o'i na Aqidu da na aiki, kuma sai mun siffantu
da kyawawan halaye da dabi'u managarta da kiyaye mutuncin mutane.
Daga zauren Dr. Aliyu Muhammad Sani