Sojojin Najeriya Sun Kashe Mataimakin Shugaban Boko Haram

A ƴan kwanakin nan sojojin Najeriya sun bayyana samun nasara a yaƙin da suke yi da ƙungiyoyin Boko Haram da ISWAP a jihar Borno.

Ko a ranar Lahadi, sojojin sun bayyana kisan Abu Khalid, “mutum na biyu mafi girman muƙami a Boko Haram a yankin dajin Sambisa,” a cewar sanarwar da sojojin suka fitar.

Sanarwar ta ce sun samu nasarar kashe Abu Khalid, da wasu mayaƙansa 10 a wani samame cikin dare da suka kai maɓoyar mayaƙan.

Kisan nasa na zuwa ne kwana daya bayan sojoji sun kawar da wani gawurtacen kwamandan Boko Haram, da ake kira Julaibib a yankin Gujba.

Ƙungiyar Boko Haram dai ta kwashe shekaru tana ƙaddamar da hare-hare kan jami'an tsaro da fararen hula musamman a yankin arewa maso gabashin Najeriya.

Tun bayan fara rikicin na Boko Haram a shekarar 2009, shugabannin ƙungiyar da suka fi kaurin suna su ne Muhammad Yusuf da ya assa ta, sai kuma Abubakar Shekau wanda ya karbi jagoranci jagorancin ƙungiyar, kafin ɓallewar tsagin ISWAP ƙarƙashin jagorancin Abu Mus’ab Al-Barnawi.

Sai dai tun bayan kisan shekau a 2021, Boko Haram da ISWAP sun ci gaba da gudanar da ayyukansu a ware, ƙarƙashin jagorancin sabbin shugabanni, wadanda a mafi yawan lokuta ba kowa ne ya san su ba.

Post a Comment

Previous Post Next Post