A yau ne aka fara aikin Hajjin shekarar 2026 a ƙasar Saudiyya a daidai lokacin da yankin ke fama da tashin hankali sakamakon yaƙin Iran.
Hukumomin Saudiyya sun ce sama da mahajjata miliyan ɗaya da rabi daga ƙasashen waje ne suka isa ƙasar domin gudanar da ibadar bana, adadin da ya zarce na shekarar da ta gabata duk da rikice-rikicen a ke ci gaba a yankin.
Rahotanni sun kuma nuna cewa Saudiyya ta fuskanci wasu hare-hare tun bayan fara yaƙi tsakanin Iran da Amurka da kuma Isra'ila, abin da ya ƙara dagula yanayin tsaro a yankin.
Domin kwantar da hankulan mahajjata, ma’aikatar tsaron Saudiyya ta fitar da bidiyo da ke nuna na’urorin kariya na sararin samaniya da aka girke a kewayen birnin Makka.
