Ana ci gaba da kaɗa ƙuri’a a zaɓen majalisar dokoki na gaggawa a Malta, yayin da rahotannin jin ra’ayin jama’a ke nuna cewa jam’iyyar Labour mai mulki na da babbar damar sake lashe zaɓen da ci gaba da riƙe mulki karo na huɗu a jere.
An buɗe rumfunan zaɓe a faɗin ƙasar da ke tsakiyar Tekun Bahar Rum, inda masu jefa ƙuri’a ke zaɓen ‘yan majalisar da za su jagoranci ƙasar na tsawon shekaru biyar masu zuwa.
Firaminista Robert Abela na jagorantar jam’iyyar Labour, yayin da jam’iyyar adawa ta Nationalist Party ke ƙarƙashin jagorancin Alex Borg.
Firaminista Abela ya kira wannan zaɓen gaggawa tun kafin cikar wa’adin gwamnati, yana mai cewa Malta na buƙatar kwanciyar hankali na siyasa a daidai lokacin da duniya ke fuskantar rashin tabbas da rikice-rikicen ƙasa da ƙasa.
Tattalin arziki ya zama babban batu a yakin neman zaɓen, inda Malta ke daga cikin ƙasashen Tarayyar Turai masu kyakkyawan ci gaban tattalin arziki tare da ƙarancin rashin aikin yi da sauƙin hauhawar farashi idan aka kwatanta da wasu ƙasashe.
Sai dai mutane da dama sun nuna damuwa kan tsadar rayuwa, tashin farashin gidaje, cunkoson jama’a, da matsin lamba kan kayayyakin more rayuwa.
Binciken jin ra’ayin jama’a da aka gudanar kafin zaɓen ya nuna jam’iyyar Labour na gaba da babbar tazara, inda wasu rahotanni suka nuna tana iya samun sama da kashi 53 cikin ɗari na ƙuri’u.
Zaɓen na gudana ne har yanzu a ƙarƙashin inuwa ta kisan fitacciyar ‘yar jarida Daphne Caruana Galizia a shekarar 2017, wanda ya tayar da muhawara kan cin hanci da rashawa da yadda ake gudanar da gwamnati a Malta.
Ana sa ran sakamakon zaɓen zai fara fitowa bayan an kammala kaɗa ƙuri’a da ƙirga ƙuri’u.