Kasar Sin Ta Buɗe Wa Kayayyakin Afirka Kasuwa, Za Ta Samar Wa Matasan Najeriya Ayyukan Yi

Jamhuriyar Jama'ar Sin ta sanar da faɗaɗa damar shigar da kayayyakin kasashen Afirka cikin kasuwanninta, tare da ƙara samar da guraben ayyukan yi ga matasan Najeriya. Wannan mataki na zuwa ne a matsayin wani ɓangare na ƙoƙarin zurfafa dangantakar dake tsakanin ɓangarorin biyu, domin ya wuce tattaunawar diflomasiyya ta al'ada.

An bayyana wannan babban kudiri ne yayin Taron Musayar Ra'ayi na Matasan Sin da Najeriya da aka gudanar a Abuja. Ofishin Jakadancin Sin da ke Najeriya ne ya shirya taron tare da haɗin gwiwar Ma'aikatar Bunƙasa Al'amuran Matasa ta Tarayya, da nufin ciyar da manufar "Gina Al'umma mai kyakkyawar makomar bai ɗaya tsakanin Sin da Afirka" gaba.

Yayin da yake jawabi a taron, Wakilin Jakadan Sin, Zhou Hongyou, ya bayyana cewa kwanan nan ƙasarsa ta soke harajin kwastam (zero tariffs) kwata-kwata a kan dukkan kayayyakin da ke fitowa daga ƙasashe 13 na Afirka masu huldar diflomasiyya da Beijing. Haka kuma, ƙasar ta inganta tsarin nan na musamman mai saurin tantance kaya (green channel) domin sauƙaƙe shigar da kayayyakin Afirka cikin kasuwar Sin cikin gaggawa.

Malam Zhou ya ƙara da cewa, an tsara waɗannan matakai ne domin ƙarfafa haɗin gwiwar tattalin arziki da kuma buɗe wa ƙasashen Afirka ƙarin damammaki a fagen kasuwancin duniya.

Daga nan sai ya yi kira ga matasan ƙasashen biyu da su rungumi manufar buɗe ƙofa ga juna da haɗa kai, inda ya jaddada cewa ya kamata a kalli haɗin gwiwar ƙasa da ƙasa a matsayin haɗin gwiwa na bai ɗaya wajen magance ƙalubalen da ke fuskantar duniya.

A cewarsa, matasa suna da gagarumar rawar da za su taka wajen dorewar tattaunawa, musayar abubuwan da aka koya na ci gaba, da kuma fassara waɗannan shawarwari su koma fa'idodi na zahiri ga zamantakewa da tattalin arzikin al'umma.

Yayin da yake wakiltar Ma'aikatar Bunƙasa Al'amuran Matasa ta Tarayya, Darakta mai kula da Ilimi da Bunƙasa Matasa, Despan Kwardem, ya jinjina wa waɗanda suka halarci taron. Ya kuma mika godiyarsa ga Babban Daraktan Hukumar Yi wa Ƙasa Rawani (NYSC) bisa tabbatar da cewa an shigar da 'yan rukunin masu yi wa ƙasa hidima cikin wannan gagarumin taro.

Post a Comment

Previous Post Next Post