Agbese Ya Bukaci Tinubu Ya Dakatar da Sauye-Sauyen NYSC Domin karin Tattaunawa

Mataimakin Kakakin Majalisar Wakilai, Philip Agbese, ya roƙi shugaban ƙasa Bola Tinubu da ya dakatar da aiwatar da sabon tsarin da gwamnatin tarayya ke shirin yi wa Hukumar Aikin Juyin Shekara ta Ƙasa (NYSC), domin a yi karin tattaunawa. 

Agbese, wanda yake wakiltar mazabar Ado/Okpokwu/Ogbadibo ta Jihar Benue, ya ce, dole ne a yi karin tattaunawa sosai kafin a fara aiwatar da canje-canjen. A cikin wata sanarwa da ya fitar jiya, dan majalisar ya ce, NYSC na daya daga muhimman cibiyoyin kasa da ta taka muhimmiyar rawa wajen inganta hadin kai da ci gaban kasa tun da aka kafa ta a shekarar 1973. Duk da yake ya amince da bukatar gyara, ya jaddada cewa canje-canjen ba za su rage asalin manufar hukumar ba, wadda ke karfafa hade-haden matasa a tsakanin al’ummar Najeriya. 

Wasu daga cikin canje-canjen da aka gabatar sun haɗa da nada babban darakta na farar hula maimakon na sojoji, sake tsara sansanin horo zuwa matakai uku, ƙirƙirar fannoni na musamman guda 11 ga 'yan NYSC, da kuma ƙarfafa shirye-shiryen samun kwarewa. Agbese ya nuna damuwa musamman kan nadin babban darakta na farar hula, yana mai cewa shugabancin sojoji ya taimaka wajen kiyaye ɗabi’a, son ƙasa, da jin aikin ƙasa a tsakanin matasa. Duk da haka, wani jagoran jam'iyyar APC, Olatunbosun Oyintiloye, ya ce wannan matakin zai inganta kokarin gwamnatin tarayya na samun tattalin arziki na dala tiriliyan guda.

Post a Comment

Previous Post Next Post