Iran ta Gargaɗi Trump ya Damu da Tsaron Kansa Maimakon Mashigar Hormuz

Shugaban Kwamitin Tsaro da Harkokin Waje na Majalisar Iran, Ebrahim Azizi, ya mayar da martani ga kalaman Donald Trump kan mashigar Hormuz, yana mai cewa shugaban na Amurka ya kamata ya damu da tsaronsa maimakon ci gaba da yin barazana game da mashigin ruwan.

Kalaman na sa sun zo ne a matsayin martani ga abin da Donald Trump ya faɗa a jiya inda ya ce zai ayyana mashigar Hormuz a matsayin na Amurka.

Daga baya fadar White House ta ce kalaman Trump shaci faɗi ce amma kalaman nasa sun jawo ce-ce-ku-ce a kafafen yaɗa labarai da kuma tsakanin jami'an gwamnati da 'yan siyasar Iran.

Mashigar Hormuz na daga cikin muhimman hanyoyin jigilar man fetur a duniya, lamarin da ke sa duk wata magana a kansa ta ja hankalin ƙasashen duniya..

Post a Comment

Previous Post Next Post