Lauyan Effiong Ya Nuna Rashin Amincewa da Gargadin IGP Kan Daukar Jami’an ’Yan Sanda a Bidiyo

Lauyan nan mai rajin kare haƙƙin bil’adama, Inibehe Effiong, ya nuna rashin amincewarsa da gargadin Babban Sufeton ’Yan Sandan Najeriya (IGP), Tunji Disu, na hana ’yan Najeriya daukar jami’an ’yan sanda a bidiyon barkwanci da ake wallafawa a kafafen sada zumunta.Effiong ya ce ita kanta Rundunar ’Yan Sandan Najeriya wata cibiya ce da ke ƙirƙirar abubuwan da ake wallafawa a kafafen sadarwa, kasancewar tana da shafukan sada zumunta, gidan yanar gizo da gidan rediyo da take amfani da su wajen samar da bayanai da yaɗa su.

Lauyan ya bayyana hakan ne a ranar Juma’a, yayin wata hira da gidan talabijin na Channels Television.

IGP Disu ya gargadi ’yan Najeriya kan ɗaukar jami’an ’yan sanda a bidiyon barkwanci, yana mai bayyana hakan a matsayin abin da ke “matuƙar karya gwiwar” jami’an rundunar.

Sai dai IGP ya bayyana cewa damuwarsa ba ta shafi haƙƙin ’yan ƙasa na ɗaukar jami’an ’yan sanda a bidiyo ba, illa dai amfani da jami’an wajen samar da abubuwan da za a wallafa a kafafen sada zumunta.

Da yake mayar da martani, Effiong ya tambayi abin da ya kamata a kira ƙirƙirar abun ciki, da kuma ko samun kuɗi ne ko wayar da kan jama’a zai zama ma’aunin tantance hakan.

Ya ce: “Mene ne ƙirƙirar abun ciki? Shin0 abubuwan da ake samarwa da yaɗawa ko wallafawa ko rarrabawa ne domin samun kuɗi? Ko kuma kawai wallafa bayanai ne domin wayar da kan jama’a? Mene ne ma’aunin tantancewa? Shin neman riba ne ko wayar da kan jama’a? Kuma wane ne mai ƙirƙirar abun ciki?”

Effiong ya ce idan aka duba ma’anar ƙirƙirar abun ciki a faɗaɗe, za a iya cewa ita ma rundunar ’yan sanda cibiya ce mai ƙirƙirar abun ciki.

Ya bayyana cewa rundunar tana da shafukan sada zumunta, gidan yanar gizo da gidan rediyo, waɗanda take amfani da su wajen samar da bayanai da yaɗa su ga jama’a.

Lauyan ya ce saboda haka ya kamata IGP ya ƙara fayyace abin da yake nufi da amfani da jami’an ’yan sanda wajen ƙirƙirar abun ciki.

Ya tambayi ko gargadin ya shafi masu shirya skit, ’yan wasan nishaɗi da masu barkwanci waɗanda suke dogaro da samar da irin waɗannan bidiyoyi domin samun kuɗin shiga.

Effiong ya kuma tambayi dalilin da ya sa rundunar ’yan sanda ke nuna damuwa a kai a kai game da ’yan ƙasa da ke ɗaukar jami’anta a lokacin da suke gudanar da ayyukansu.

IGP Disu ya bayar da misalan jami’an da ake ɗauka bidiyo a lokacin da suke cin abinci, yana mai bayyana hakan a matsayin ɗaya daga cikin abubuwan da ke damun rundunar.

Sai dai Effiong ya ce bai ga wata hujja da ke nuna cewa irin wannan ɗabi’a ta zama ruwan dare a kafafen sada zumunta ba.

Ya ce zai yi farin ciki idan rundunar ’yan sanda ta gabatar da misalai da za su tabbatar da irin abubuwan da IGP yake magana a kansu.

Lauyan ya jaddada cewa ’yan Najeriya suna da haƙƙin kundin tsarin mulki na ɗaukar jami’an tsaro a lokacin da suke gudanar da ayyukansu na doka a wuraren da jama’a ke iya gani.

Ya ce wannan haƙƙi yana ƙarƙashin Sashe na 39 na Kundin Tsarin Mulkin Tarayyar Najeriya na 1999, wanda ya tanadi ’yancin faɗar albarkacin baki.

A cewarsa, wannan ’yancin ya haɗa da damar yaɗawa da isar da ra’ayoyi da bayanai ga jama’a.

Ya ƙara da cewa kariyar kundin tsarin mulkin ta shafi hanyoyin da ake amfani da su wajen yaɗa bayanai, ciki har da wayoyin hannu da sauran na’urorin lantarki.

Effiong ya ce, a ƙarƙashin tsarin kundin tsarin mulkin da ake da shi a yanzu, haƙƙin kowane mutum na ɗaukar jami’an gwamnati a wuraren da jama’a ke iya gani yayin da suke gudanar da ayyukan hukuma, muhimmin haƙƙi ne.

Post a Comment

Previous Post Next Post