Sheikh Ahmad Mahmud Gumi Ya Bukaci Gwamnatin Jihar Kano Da Ta Saki Sheikh Abduljabbar Nasiru Kabara Da Ke Tsare A Gidan Gyaran Hali

 Kamar yadda jaridar Mikiya ta ruwaito, fitaccen malamin addinin Musulunci, Sheikh Ahmad Gumi, ya shawarci gwamnatin jihar Kano da ta saki Sheikh Abduljabbar Nasiru Kabara tare da daina kame-kamen malamai a jihar. Sheikh Gumi ya ce "ya kamata gwamnati ta samar da tsari na baiwa kowa ‘yancin yin wa’azi cikin hikima da lumana, domin gujewa rikice-rikice da hana walwalar addini."

Sheikh Ahmad Gumi

Sheikh Abduljabbar Nasiru Kabara ya shafe kusan shekaru huɗu yana tsare a gidan yari tun lokacin gwamnatin Dr. Abdullahi Umar Ganduje, bayan gurfanar da shi a gaban kotu bisa zargin ɓatanci ga Annabi Muhammadu (SAW). Sheikh Gumi ya jaddada cewa kawo ƙarshen takurawa malaman addini zai taimaka wajen samar da zaman lafiya da fahimtar juna a Kano da Najeriya baki ɗaya.

Post a Comment

Previous Post Next Post