Atiku, Obi, Amaechi: Wane ne Zai yi Wa ADC Takarar Shugaban Kasa a 2027?

A ranar Laraba ta jajiberin sabuwar shekarar 2026 ne tsohon gwamnan jihar Anambra wanda kuma ya yi takarar shugabancin Najeriya a jam'iyyar Labour a 2023, Peter Obi ya sanar da komawarsa jam'iyyar haɗaka ta ADC.

Tsohon mataimakin shugaban Najeriya, Atiku Abubakar ne ya bayyana haka a wani saƙo da ya wallafa a shafukansa na sada zumunta, inda ya ce komawar Obi jam'iyyar wani babban mataki ne mai muhimmanci a tarihin haɗaka a siyasar Najeriya.

"Ina maraba da komawar Peter Obi cikin jam'iyyar ADC a hukumance, wanda yake cikin ƙoƙarin da muke na samar da haɗaka mai ƙarfi da za ta ƙalubalanci jam'iyya mai mulki. Jam'iyyar da za ta kafa mulkin da zai tabbatar da zaman lafiya da cigaban ƙasa."

Atiku ya ce yana fata komawar Obi cikin jam'iyyar za ta buɗe ƙofar da wasu waɗanda ya bayyana da 'masu kishi' za su biyo domin shiga jirgin haɗakar.

Ƴan Najeriya dai na yin tambayar cewa wane ne a cikin jiga-jigan ƴan siyasar da ke cikin jam'iyyar ta haɗaka zai yi wa jam'iyyar takarar shugaban ƙasa domin ƙalubalantar shugaba Bola Tinubu na jam'iyya mai mulki ta APC a 2027.

Tsohon mataimakin shugaban Najeriya, Atiku Abubakar wanda ya yi takarar neman shugaban ƙasa karo huɗu da Peter Obi wanda ya yi takarar shugaban ƙasa a jam'iyyar LP a 2023 da tsohon gwamnan jihar Ribas, Rotimi Amaechi tare da wasu gaggan ƴan hamayya su ne fuskokin da aka gani a haɗakar.

Haɗakar ƴan siyasar dai ta tayar da hankalin jam'iyya mai mulki da ma sauran jam'iyyun hamayya, inda masana da ƴan ƙasar ke hasashen rashin jin daɗin jam'iyyun ba zai rasa nasaba da irin ƙalubalantar su da haɗakar za ta yi ba a 2027.

To sai dai furucin da jiga-jigan ƴan hamayyar ke yi dangane da sha'warsu ta tsaya takarar shugaban ƙasa a sabuwar jam'iyyar ta haɗaka na dasa ayar tambaya dangane da ƙarkon da haɗakar ka iya yi.


Post a Comment

Previous Post Next Post