'Allah Ya Kone Kauyenku’: Gangamin Tutar Isra’ila Ya Koma Gabashin Kudus

Dubban masu kishin ƙasar Isra’ila sun gudanar da gangamin tutar Isra’ila a Gabashin birnin Kudus, wani taro na shekara-shekara da ya sake tayar da hankali a birnin da ake taƙaddama a kansa.

Isra’ila

A yayin gangamin, an rahoto cewa wasu mahalarta taron na rera kalamai masu tunzura jama’a irin su “Allah ya ƙone ƙauyenku” tare da wasu maganganun ƙyamar Larabawa yayin da suke wucewa ta unguwannin Falasɗinawa da ke tsohon birnin Gabashin Kudus. Ana gudanar da wannan gangami ne domin tunawa da yadda Isra’ila ta ƙwace Gabashin Kudus a yaƙin Gabas ta Tsakiya na shekarar 1967.

Jami’an ‘yan sanda na Isra’ila da yawa sun bazu a sassan birnin domin tabbatar da tsaro da kuma hana rikici tsakanin mahalarta gangamin da Falasɗinawa mazauna yankin. Rahotanni sun nuna cewa an samu saɓani da cacar baki a wurare daban-daban, yayin da aka tilasta wa wasu ‘yan kasuwar Falasɗinu rufe shaguna saboda hanyar da gangamin ya bi.

Shugabannin Falasɗinawa da ƙungiyoyin kare haƙƙin ɗan adam sun yi Allah-wadai da gangamin, suna zargin mahalarta taron da ƙoƙarin tunzura mazauna yankin da kuma ƙara tsananta rikici a birnin.

Sai dai jami’an Isra’ila sun kare gangamin, suna cewa wani ɓangare ne na bikin ƙasa kuma yana ƙarƙashin ‘yancin gudanar da taro cikin lumana.

Gabashin Kudus na ci gaba da kasancewa ɗaya daga cikin wuraren da ake taƙaddama a kai sosai a rikicin Isra’ila da Falasɗinu. Falasɗinawa na son yankin ya zama babban birnin ƙasarsu a nan gaba, yayin da Isra’ila ke kallon dukkanin Kudus a matsayin babban birninta, duk da cewa ƙasashe da dama ba su amince da hakan ba.

Post a Comment

Previous Post Next Post