Hare-hare da tarzoma kan cibiyoyin kula da masu cutar Ebola sun ƙaru a gabashin Democratic Republic of the Congo yayin da hukumomin lafiya ke ƙoƙarin shawo kan ɓarkewar cutar da ke haifar da fargabar yaɗuwarta a yankin.
Rahotanni sun bayyana cewa wasu fusatattun mazauna yankuna sun kai hari tare da ƙona wasu cibiyoyin kula da masu cutar Ebola saboda rashin yarda da matakan da jami’an lafiya ke ɗauka, musamman kan yadda ake binne gawarwaki da kuma killace marasa lafiya.
A wani hari da aka kai a yankin Mongbwalu, mutane sun ƙona tantunan jinya na wata cibiyar da ƙungiyar Doctors Without Borders ke gudanarwa, lamarin da ya sa wasu da ake zargin suna ɗauke da cutar suka tsere daga wurin.
Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ta bayyana cewa sabon ɓarkewar cutar Ebola mai nau’in Bundibugyo ya zama babban haɗari ga yankin, musamman saboda babu ingantaccen rigakafi ko magani da aka amince da shi ga wannan nau’in cutar. Hukumar ta kuma ce rikice-rikice, rashin tsaro, da ƙarancin kayan aikin lafiya na hana jami’ai shawo kan cutar yadda ya kamata.
Masana lafiya sun yi gargadin cewa rashin amincewa tsakanin jama’a da hukumomi na iya ƙara sa cutar ta bazu cikin sauri, musamman a yankunan da ake fama da rikicin ‘yan bindiga da yawan ƙaura.
Tun bayan sanar da sabon ɓarkewar cutar a watan Mayu, an ruwaito ɗaruruwan waɗanda ake zargi sun kamu da Ebola tare da mutuwar mutane da dama a gabashin Congo da wasu sassan Uganda.