Sanata Bill Cassidy na jam’iyyar Republican daga jihar Louisiana na fuskantar matsin lamba daga masu goyon bayan shugaban Amurka Donald Trump, yayin da ake tunkarar zaɓen fidda gwani na jam’iyyar a jihar. Dalilin hakan shi ne kuri’ar da Cassidy ya kaɗa a shekarar 2021 domin a hukunta Trump a shari’ar tsige shi karo na biyu.
Cassidy na daga cikin sanatocin Republican bakwai da suka goyi bayan hukunta Trump bayan harin da aka kai Majalisar Dokokin Amurka a ranar 6 ga Janairu, 2021. Wannan mataki ya fusata magoya bayan Trump sosai, har jam’iyyar Republican ta jihar Louisiana ta fitar da sanarwar Allah-wadai da Cassidy bayan kuri’ar.
Yanzu da Cassidy ke neman sake komawa Majalisar Dattawan Amurka, yana fuskantar ƙalubale daga ‘yan takarar da Trump ke marawa baya, ciki har da ‘yar majalisar wakilai Julia Letlow da tsohon ɗan majalisa John Fleming. Trump ya fito fili ya nuna goyon bayansa ga Letlow, lamarin da ya mayar da zaɓen Louisiana wata muhimmiyar gwaji ga tasirin Trump a cikin jam’iyyar Republican.
Masu sharhi kan siyasa sun bayyana cewa kuri’ar da Cassidy ya kaɗa kan Trump har yanzu tana daga cikin manyan batutuwan da ke tasiri a yakin neman zaɓensa, musamman tsakanin masu ra’ayin mazan jiya masu biyayya ga Trump.
Ana sa ran gudanar da zaɓen fidda gwani na Republican a Louisiana a ranar 16 ga Mayu, kuma ana kallon sakamakon a matsayin wata alama ta irin ƙarfin da Trump ke da shi a cikin jam’iyyar Republican kafin zaɓen tsakiyar wa’adi na shekarar 2026.