Wani lamari mai ban mamaki da ya jawo ce-ce-ku-ce a Kano ya kai ga cafke mutane huɗu bayan zargin wani matashi da yanke yatsarsa don kai wa boka, bisa alƙawarin samun kuɗi har naira miliyan 80.
Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta ce bincikenta ya gano cewa matashin ya aikata hakan ne bayan an yi masa alƙawarin samun ɗimbin kuɗi, amma daga bisani ya ce bai samu kuɗin da aka yi masa alƙawari ba.
Kakakin rundunar 'yan sandan jihar, CSP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya shaida wa BBC yadda lamarin ya faru, yana mai cewa bincike ya kai ga gano wasu da ake zargin suna da hannu a wannan al'amari.
A yayin binciken, matashin da ake zargi da kuma bokan sun yi bayani kan abin da suka ce ya faru, inda kowannensu ya bayyana nasa ɓangaren labarin dangane da zargin da ake yi.
